Dalibai ‘yan asalin jihar Kano dake karatu a Jami’ar tarayya dake Dutsen jihar Jigawa sunyi kira ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya kai musu dauki ta hanyar tallafasu da kudin makaranta.
“makaranta ta baiwa dalibai damar biyan kudin kowane zangon karatu maimakon biya a dunkule.
To mun biya na zangon farko kaso sittin yanzu na zango na biyu zamu biya wanda shine kaso arba’in,” a cewar sa.
Kungiyar daliban ‘yan asalin jihar Kano dake karatu a Dutsen jihar Jigawa ta bukaci gwamnan da ya duba koken su domin kai musu dauki duba da cewa da yawa zasu iya ajiye karatun su.