Type Here to Get Search Results !

Ads

Dalibai ‘yan asalin Kano dake karatu a jami’ar tarayya dake Dutse a Jigawa sun roki gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya biya musu kudin makaranta

Top Post Ad

Dalibai ‘yan asalin jihar Kano dake karatu a Jami’ar tarayya dake Dutsen jihar Jigawa sunyi kira ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya kai musu dauki ta hanyar tallafasu da kudin makaranta.

“makaranta ta baiwa dalibai damar biyan kudin kowane zangon karatu maimakon biya a dunkule.

To mun biya na zangon farko kaso sittin yanzu na zango na biyu zamu biya wanda shine kaso arba’in,” a cewar sa.

Kungiyar daliban ‘yan asalin jihar Kano dake karatu a Dutsen jihar Jigawa ta bukaci gwamnan da ya duba koken su domin kai musu dauki duba da cewa da yawa zasu iya ajiye karatun su.

Kaso 60 na dalibai ne suka ci jarrabawa a bana-NECO
Idan za a iya tunawa a makonin da suka gabata ne dai gwamna Abba Kabir Yusuf, ya dauki nauyin biyawa dalibai ‘yan asalin jihar Kano dake karatun digirin farko kudin makaranta na Jami’ar Bayero.

Below Post Ad

Tags

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Listen Freedom Radio Live (PRO)

Freedom Radio Kano 99.5 FM

Freedom Radio Kaduna 92.9 FM

Freedom Radio Dutse 99.5 FM

Dala FM Kano 88.5

Hollywood Movies